Connect with us

Labarai

Dakatar da layukan sadarwa ya rage yawan hare-hare a jihar Zamfara

Published

on

A kwana-kwanan nan ne jihar Zamfara ta ɗauki sabbin matakai domin yaƙi da matsalar tsaro ciki kuma har da rufe layukan waya.

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Muhammad Matawalle ya bayyawa Freedom Radio cewa matakin toshe layukan wayar, zai sa ƴan bindigar a mawuyacin hali, ta yadda jami’an tsaro zasu samu damar zaƙulo ƴan ta’addan.

Matawalle ya ce “lalle an samu cigaba ƙwarai da gaske tunda har an, raunata wasu an kuma kashe wasu, kuma nan bada dadewa ba za’a kawo ƙarshen duk wasu hare-hare a fadin jihar”.

Wani mazauni yankin karkara daga ƙaramar hukumar Tsafe, mai suna Bashar Fegin Ɗanmarke ya ce “ kusan sati guda kenan yanzu mun samu nutsuwa da kwanciyar hankali.”

Shima wani direba mai suna Nura Ibrahim ya ce lallai dokokin sunyi tasiri ƙwarai da gaske, tunda gashi har ƴan bindikar sun sallamo mutanan su kusan su ashirin ba tare da an basu ko sisi ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!