Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Tsaro: Dokar katse layukan waya na nan daram a Zamfara – Gwamna Matawalle

Published

on

Gwamnatin jihar Zamfara ta ce, za a ci gaba da zama cikin dokar katse layukan waya.

Gwamnan jihar Muhammad Bello Matawalle ne ya bayyana hakan a zantawar sa da BBC Hausa.

Ya ce, za a ci gaba da zama ƙarƙashin dokar har sai lokacin da jami’an tsaro suka bada rahoto mai kyau ga me da yaƙi da ayyukan tsaro.

Ƴan bindiga sun ƙone gidan shugaban majalisar dokokin jihar Zamfara  

Matawalle ya kuma ce, a yanzu ana ganin amfanin datse layukan wayar musamman yadda ƴan bindaga suke bayyana kan su sakamakon matsin da suka shiga.

Rahotanni sun tabbatar da cewa, yanzu haka al’umma jihar Zamfara na fita zuwa jiha Sokoto da Funtua a jihar Katsina don yin kiran waya ko aika gajeren saƙo da sauran buƙatun su a wayar.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!