Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Dantakarar gwamnan Ekiti ya shigar da kara Kayode Fayemi gaban kotu

Published

on

Dantakarar gwamnan jihar Ekiti a jam’iyya APC Segun Oni ya shigar da wata kara gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja inda yake kalubalantar tsayar da Kayode Fayemi a matsayin dan takarar jam’iyyar APC da ta tsayar a zaben ranar 14 ga watan Yuli mai zuwa.

 

Oni ya shigar da wannan karar ne gaban babbar kotun tarayyar ta hannun lauyansa Gani Faniyi.

 

Kayode Fayemi wanda ya samu kuri’u 941 a zaben fidda gwani da jam’iyyar APC ta gabatar a ranar 12 ga watan Mayun da ya gabata ya samu nasara ne akan Oni wanda ya samu kuri’u 460.

 

Sai dai Oni ya bukaci kotu da ta tabbatar masa cewar ko ya halarta Fayemi ya tsaya takarar, duk da cewa a lokacin da a aka gudanar da zaben bai yi murabus daga kan mukamin sa na minista ba ko kuma aka sin haka.

 

Haka kuma ya bukaci kotun da ta tabbatar masa cewar ko bashi takarar ya sabawa kundin tsarin mulkin kasa da kuma tsarin da jam’iyyar ta APC ke tafiya a kai.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!