Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Dokar tanadin kalubalen lafiya da ka iya tasowa ta tsallake karatu na biyu

Published

on

Dokar Tsaron ƙalubalen lafiya da ka iya tasowa ta Bana, ta tsallake karatu na biyu a majalisar dokokin jihar Kano.

Dokar ta kai wannan mataki ne yayin zaman majalisar na yau ƙarƙashin jagorancin shugabanta Jibril Isma’il Falgore.

A zaman na yau, Ɗan majalisar dokokin mai wakiltar ƙaramar hukumar Takai Dakta Musa Ali Kachako ne ya gabatar da karatu na biyu wanda bayan tattaunawa a tsakanin mambobin majalisar suka amince da karatun nasa.

A ganawar sa da manema labarai, Ɗan majalisar na Takai, ya bayyana wasu cikin alfanun da samar da dokar zai haifar.

A wani labarin kuma, majalisar ta buƙaci gwamnatin jiha da ta samar da tsaftataccen ruwan amfanin yau da kullum a yankin ƙaramar hukumar Tudun Wada.

Majalisar ta buƙaci hakan ne biyo bayan ƙudurin da wakilin ƙaramar hukumar Tudun Wada Sule Lawan ya gabatar yayin zaman na yau.

Ɗan majalisar ya ce, wahalar ruwa a yankin ta sanya har ana sayar da Lita 25 ta Ruwa a kan Naira 100.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!