Connect with us

Labarai

Dole ne a bai wa bangaren shari’a na jihohi cikakken ‘yanci – Majalisar Dattijai

Published

on

Majalisar dattijai ta shaidawa gwamnonin kasar nan cewa, bai wa bangaren shari’a na jihohi cikakken ‘yancin sarrafa kudaden su lamari ne da ya zama dole da babu wanda zai canja shi.

 

Shugaban kwamitin kula da harkokin shari’a da kare hakkin bil adama na majalisar dattawa, Sanata Opeyemi Bamidele ne ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai a Abuja.

 

Ya ce, abin kunya ne ace a wannan lokaci bangaren shari’a na jihohi na karkashin ikon gwamnonin, saboda haka majalisar dattijai za ta ci gaba da bai wa bangaren shari’a na jihohi goyon bayan da suke bukata don cimma muradun su.

 

A baya-bayan nan ne dai kungiyar ma’aikatan bangaren shari’a suka fara wani yajin aiki don nuna adawa da ci gaba da dakile bangaren shari’a na jihohi da su ke zargin gwamnoni na yi.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!