Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yajin aiki: majalisar wakilai ta goyi bayan bai wa bangaren shari’a ‘yancin cin gashin kai

Published

on

Majalisar wakilan Najeriya ta goyi bayan kudirin bai wa bangaren shari’a ‘yancin cin gashin kai, wanda hakan zai bai wa bangaren shari’a damar yin aiki ba tare da tsangwama ba.

Kwamitin majalisar kan harkokin shari’a ya bayyana hakan ne a ganawar sa da mambobin kungiyar ma’aikatan bangaren shari’a ta kasa jiya a Abuja.

Shugaban kwamitin, Onofiok Luke, ya ce majalisar ta goyi bayan su ne, sakamakon yadda bangaren shari’ar ke da matukar muhimmanci ga dorewar dumokradiyya da ayyukan bangarorin gwamnati uku.

A cewar kwamitin majalisar, yana bukatar samun karin bayani daga kungiyar lauyoyin don lalubo hanyoyin magance matsalar su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!