Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Dr Sa’idu Ahmad Dukawa; an sami cigaba a demokradiya a kasar nan

Published

on

Masanin nan kan harkokin kimiyyar Siyasa kuma Malami a Jami’ar Bayero da ke nan Kano Dokta Sa’idu Ahmad Dukawa, ya bayyana cewar an samu ci gaba a Dimokoradiyyar kasar nan ta fannin tattalin arziki da tsaro, duk da cewar akwai yan rikice-rikice a cikin siyasar.

Dokta Sa’idu Ahmad Dukawa ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala Shirin Barka Da Hantsi na nan Freedom Rediyo na yau.

Sa’idu Ahmad Dukawa ya kuma ce rikicin da ke faruwa tsakanin jam’iyyun a Jihohin kasar nan ba zai haifar da wata matsala ga Dimokoradiyyar kasar nan ba, duba da yadda zabe ke gabatowa.

Dakta Sa’idu Ahmad Dukawa ya shawarci shugabanin jam’iyyu da su yi duk abinda ya kamata wajen tafiyar da jam’iyyun na su, tare da gujewa haddasa rikice-rikicen da za su iya janyo zubar da jini yayin zabe don ganin an kara bunkasa Dimokoradiyyar kasar nan.

A na sa bangaren shugaban Jam’iyyar APC a Jihar Kano Abdullahi Abbas cewa ya yi an samu ci gaba matuka a Dimokradiyyar a Jihar Kano da ma kasa baki-daya, inda ya bada misalin cewa a Kano shugaban Jam’iyyar yana samun girmamawar da ta kamata daga wajen gwamna da sauran mambobin Jam’iyya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!