Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

DSS:ta sako magoya bayan akidar Kwankwasiya su biyu

Published

on

Hukumar tsaron sirri ta DSS ta sako daya daga cikin magoya bayan akidar siyasar Kwankwasiyya mai suna Salisu Hotoro da Babangida da akewa lakabi da Bangis wadanda ta kama a kwanakin baya, bayan sun kwashe tsawon kwanaki goma sha biyu.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai magana da yawun dan takarar gwamnan jihar Kano karkashin jam’iyyar PDP Sanusi Bature Dawakin-Tofa.

 

Sanarwar ta ce jami’an hukumar tsaron sirri ta DSS ne suka kama mutanen biyu makwanni biyu da suka gabata, bisa zargin da su kansu ba a sanar da su ba.

 

A cewar sanarwar, sakamakon rashin hujjoji da hukumar ta DSS ke da shi kan mutanen biyu, ya sanya ta gaza gurfanar da su gaban kotu.

 

Sanusi Bature Dawakin-Tofa ta cikin sanarwa dai, ya kara da cewa, jam’iyyar PDP, za ta zauna don daukar mataki na gaba game da shirin ta na gudanar da zanga-zangar lumana a gobe Alhamis, wanda ta shirya tun da fari za ta yi, da nufin nuna adawa da cin zarafin ‘ya’yan jam’iyyar da jami’an tsaro ke yi a jihar Kano.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!