Connect with us

Labarai

ECOWAS za ta yi taro bisa ficewar Nijar Mali da Burkina Faso daga kungiyar

Published

on

Kungiyar tattalin arzikin ƙasashen Afrika ta yamma, ECOWAS, ta bayyana cewa za ta gudanar da taro na musamman, kan ficewar ƙasashen Nijar da Mali da kuma Burkina Faso daga ƙungiyar.

A cewar ECOWAS ta cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, za ta yi taron ministocin ƙungiyar ne a Accra, babban birnin ƙasar Ghana.

BBC, ta ruwaito cewa, wasu majiyoyi sun ce taron zai tattauna hanyoyin ficewar ƙasashen daga ƙungiyar da kuma tasirin hakan a kan hukumomi da cibiyoyin ƙungiyar da ke ƙasashen uku.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!