Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Dage takunkumi zai habaka tattalin yammacin Afrika- Sanatocin Arewa

Published

on

Kungiyar Sanatocin Arewa ta yabawa ƙungiyar raya tattalin arzikin kasashen Afrika ta ECOWAS, sakamakon janye jerin takunkuman da ta ƙaƙabawa ƙasashen Nijar Da Burkina Faso, da kuma Mali sakamakon Juyin mulkin da akayi a kasashen.

Wannan na cikin wata sanarwa da Mai magana da yawun ƙungiyar, kuma sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Abdruhaman Kawu Sumaila ya sanyawa hannu.

Sanarwar ta kuma ce janye takunkuman da ECOWAS ta yi wa kasashen ya sake tabbatar da aniyar ƙungiyar na samar da dai-dai to da kuma ciyar da yankin Afrika ta yamma gaba.

A jiya Asabar ne dai ƙungiyar ECOWAS, ta sanar da janye takunkuman da ta ƙaƙabawa ƙasashen Nijar da Burkina Faso da Mali, a taron da tayi a Abuja, da ta ce ta ɗauki matakin ne a wani yunkuri na sauƙaƙawa Al’ummar ƙasashen ƙuncin rayuwar da suka shiga la’akari da tunkarowar watan Azumin Ramadana.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!