Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Nijeriya ta damu kan matakin da Nijar da Mali da Burkinafaso suka ɗauka

Published

on

Gwamnatin tarayyar Nijeriya, ta bayyana damuwarta dangane da matakin fita da kasashen Nijar da Mali da kuma Burkinafaso suka yi daga Ƙungiyar Ecowas.

Hakan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa d mai magana da yawun ma’aikatar kula da harkokin wajen Francisca Omayuli, ta fitar da yammacin jiya Talatar makon nan.

Sanarwar ta ce, yanzu haka Nijeriya na tuntubar dukkan kasashen da ke cikin kungiyar Ecowas, domin warware matsalolin da ake fuskanta a kasashen da aka yi juyin mulki.

Haka kuma, sanarwar ta kara da cewa kofa a bude ta ke ga kasashen na Burkina Faso da Mali da Nijar ta yadda daukacin al’ummar yankin za su ci gaba da cin moriyar tattalin arziki da kimar dimukuradiyya da kungiyar ECOWAS ta amince da su.

Sanarwar ta kuma bukaci kasashen duniya da su ci gaba da bayar da goyon baya ga kungiyar ECOWAS domin samun hadin kai dangane da tsare-tsaren ƙungiyar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!