Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

EFCC ta cafke mutane 26 da ake zargi da damfara ta Internet

Published

on

Jami’an hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC shiyyar birnin Fatakwal ta ce, ta cafke mutane 26 da ake zargi da damfara ta kafar internet.

Hukumar ta EFCC ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da ta wallafa a shifinta X.

EFCC ta ce, an kama mutanen ne sakamakon sahihan bayanan sirri kan zargin da ake musu na hannu a ayyukan da suka shafi damfara ta internet.

Haka kuma ta ce, kayayyakin da aka ƙwace a hannun su sun haɗa da wayoyin hannu da kwamfutoci da motocin alfarma guda 6.

Ta cikin sanarwar, hukumar ta kuma bayyana cewa, za ta gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike a kansu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!