Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

EFCC ta fara shirin gurfanar da Murja Ibrahim Kunya a Kotu

Published

on

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC, ta ce, ta shirye-shiryen gurfanar da Murja Ibrahim Kunya a gaban kotu bayan da ta sake cafke ta sakamakon tserewar da ta yi bayan da hukumar ta bayar da ita beli tun a watan Janairun bana.

Hukumar ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da ta fitar a ya Litinin ta na mai cewa a baya ta bayar da Murja beli ne gabanin gurfanar da ita a gaban babbar kotun tarayya, amma sai ta tsere.

Haka kuma, sanarwar ta kara da cewa, tun a cikin watan Janairu ne hukumar ta kama Murja Kunya bisa zarginta da wulakanta takardun kudi, wanda hakan ya saba da dokar babban bankin kasa CBN.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!