Connect with us

Labarai

ENDSARS: ‘Yan sanda sun kama mutane 55 a kano

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama mutane 55 wadanda ake zargi da tayar da rigima a Sabon gari yayin zanga-zangar ENDSARS.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Kano DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya bayyanawa wakiliyar Freedom Radio Aisha Shehu Kabara a lahadin nan.

Ya ce, wadanda ake zargi din an kama su da laifin fasa shagunan mutane ciki har da wadanda suke dauke da makamai wanda ya hadar da bindiga da wukake.

DSP Abdullahi Kiyawa ya ce, al’ummar jihar Kano sun bai wa rundunar ‘yan sanda hadin kai a yayin da suke gudanar da zanga-zangar ENDSARS.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!