Connect with us

Labaran Wasanni

Erik ten Hag ya zama sabon mai horar da Manchester United

Published

on

Erik ten Hag zai jagoranci kungiyar kwallon kafa ta Manchester United a kakar wasanni mai zuwa.

Tawagar ce dai ta sanar da nadin sabon mai horarwar a ranar Alhamis 21 ga Afrilun 2022.

Mai shekara 52 ya amince da sanya hannu a kwantaragin shekaru 3 a kungiyar.

Dan kasar Holland ya zama mai horarawa na biyar da zai kasance a filin Old Trafford tin bayan da Alex Ferguson ya yi murabus a kungiyar a shekara 2013.

Ten Hag shi ne mai horar da Ajax, inda ya jagoranci kungiyar lashe gasar Red Devilsand.

Yanzu haka Ralf Rangnick shi ne ke rike da kungiyar a matsayin na rikon kwarya, kafin daga bisani ta sanar da sabon mai horarwa da zai kasance a kakar wasannin shekarar 2022/2023.

Manchester United dai na mataki na 6 a gasar Firimiya da maki 54 wadda ta ke yunkurin kasancewa cikin kungiyoyin da zasu wakilci kasar a gasar cin kofin zakarun turai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!