Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Erik ten Hag ya zama sabon mai horar da Manchester United

Published

on

Erik ten Hag zai jagoranci kungiyar kwallon kafa ta Manchester United a kakar wasanni mai zuwa.

Tawagar ce dai ta sanar da nadin sabon mai horarwar a ranar Alhamis 21 ga Afrilun 2022.

Mai shekara 52 ya amince da sanya hannu a kwantaragin shekaru 3 a kungiyar.

Dan kasar Holland ya zama mai horarawa na biyar da zai kasance a filin Old Trafford tin bayan da Alex Ferguson ya yi murabus a kungiyar a shekara 2013.

Ten Hag shi ne mai horar da Ajax, inda ya jagoranci kungiyar lashe gasar Red Devilsand.

Yanzu haka Ralf Rangnick shi ne ke rike da kungiyar a matsayin na rikon kwarya, kafin daga bisani ta sanar da sabon mai horarwa da zai kasance a kakar wasannin shekarar 2022/2023.

Manchester United dai na mataki na 6 a gasar Firimiya da maki 54 wadda ta ke yunkurin kasancewa cikin kungiyoyin da zasu wakilci kasar a gasar cin kofin zakarun turai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!