Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Everton ta gabadar da Lampard a matsayin sabon mai horarwa

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Everton ta gabatar da Frank Lampard a matsayin sabon mai horar da tawagar.

Everton dai ta sanar da hakane a ranar Litinin 31 ga Janairun 2022, wanda ya amince da sanya hannu a kwantaragin shekaru biyu da rabi.

Lampard tuni ya kasance a filin wasan kungiyar tin bayan da ya kasance ba shida kungiyar da ya ke jagoranta tsahon shekara guda.

Tsohon dan wasan kasar Ingila zai fara jagorantar
Everton a ranar Asabar mai zuwa a wasan da zasu kece raini da Brentford a wasa zagaye na hudu a gasar FA Cup.

Mai shekaru 43 ya maye gurbin mai rikon kwarya na kungiyar Duncan Ferguson da kuma Vítor Pereira wadanda suka jagoranci kungiyar a baya.

Kawo yanzu dai Lampard zai ci gaba da jagorantar Everton wadda maki hudu ne kacal tsakaninta da kungiyar da ke shirin fadawa a ji na biyu a gasar Firimya.

Haka kuma Lampard zai zama mai horarwa na bakwai cikin shekaru shida baya da suka taba jagorantar kungiyar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!