Connect with us

Labarai

Fadar shugaban ƙasa ta caccaki Atiku

Published

on

Fadar Shugaban Ƙasa ta soki tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar, bisa kalaman sa na cewar  ’yan Najeriya na fama da yunwa da kuma tashin hankali, da ya kwatanta halin da ake ciki a kasar  da juyin juya halin Faransa na 1789 da na Rasha na 1917.

Mai ba wa shugaban ƙasa shawara kan harkar yada labarai  Bayo Onanuga, ya ce maganganun na  Atiku ba daidai ba ne, kasar  na samun ci gaba a ƙarƙashin Shugaba Bola Tinubu.

Hadimin ya kafa  misali da yadda bayanan Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa NBS da suka nuna farashin kaya na sauka tsawon watanni biyar a jere, da ya ce  ajiyar kuɗaɗen ƙasar a waje ya haura kusan dala biliyan 42, daga biliyan 32 lokacin da Tinubu ya hau mulki.

Fadar Shugaban Ƙasa ta ce yanzu jihohi na iya biyan albashi da fansho a kan lokaci, sannan suna da rarar kuɗi don ayyukan raya ƙasa, abin da ba a saba gani ba a baya.

Fadar Shugaban Ƙasa ta kuma zargi Atiku da jam’iyyar PDP da yaɗa maganganun da za su kawo tashin hankali, da ta  bayyana cewa yawancin matsalolin da ake fuskanta sun samo asali ne daga rashin kyakkyawan shugabanci tun a lokacin PDP, lokacin da Atiku yake mataimakin shugaban ƙasa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!