Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ba a haifi Atiku a Najeriya ba, bai cancanci tsayawa takarar shugaban kasa ba – Malami

Published

on

Atoni janar na kasa kuma ministan shari’a Abubakar Malami ya shaidawa babbar kotun tarayya da ke Abuja cewa, tsohon mataimakin shugaban kasa Alhaji Atiku Abubakar bai cancanci ya sake tsayawa takarar shugaban kasa ba saboda ba a haifeshi a Najeriya ba.

 

A cewar Abubakar Malami, idan aka yi duba ga tanade-tanade da ke cikin kundin tsarin mulkin kasar nan kotun za ta amince cewa Atiku Abubakar bai cancanci tsayawa takarar shugaban kasa ba.

 

Ministan na shari’a ya ce kasancewa ba a haifi shi (Atiku) a Najeriya ba hakama mahaifansa saboda haka bai cika ka’idojin da sashe na 25 (1) da kuma (2) da kuma 131 (a) na kundin tsarin mulkin kasar nan.

 

Atoni janar na kasar ya kara shaidawa kotun cewa matukar Atiku ya tsaya takarar shugaban kasa matakin ya sabawa sashe ne 118 (1)(k) na dokokin zaben kasar nan.

 

Abubakar Malami y aba da wannan bahasi kan karar da wata kungiya wata mai suna MENA ta shigar gaban kotun ta bukatar kotun da ta haramtawa Atiku Abubakar tsayawa takarar shugaban kasa a babban zaben kasa da za ayi a shekarar 2023.

 

Ministan shari’ar ya kuma ce ko da yake dokar da ta bai wa al’ummomin arewacin Kamaru zama ‘yan Najeriya a 1961, bai bayyana cewa idan suka zama ‘yan Najeriyar daidai yake da an haife su a Najeriya ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!