Labarai
FIFA ta ɗage wasannin share fagen halartar gasar cin ƙofin duniya ɓanbagen nahiyar afurka
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/05/dlo8joqkdbb8tvrrl38m.jpg)
Hukumar ƙwallon kafa ta duniya FIFA) ta ɗage wasannin share fagen halartar gasar cin ƙofin duniya ta shekarar 2022 ɓangaren nahiyar afurka wanda aka tsara tun farko za ayi a watan yunin bana.
A yanzu dai hukumar ta FIFA ta ce za ayi wasanne a watan Satumban bana sakamakon ci gaba da fama da ake yi da cutar corona.
Haka zalika FIFA ta kuma bayyana rashin kyawun filayen wasanni a matsayin daya daga cikin dalilan
Bugu da kari, hukumar FIFA ta kara da cewa a watan Satumba, Oktoba da kuma Nuwamba za a fafata a wasanni tsakanin kasashen nahiyar da ke son halartar gasar ta cin ƙofin duniya
You must be logged in to post a comment Login