Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

KannyWood

Fim din ‘yan Shi’a : Yakubu Muhammed ya nemi afuwa

Published

on

Fitaccen jarumin nan na masana’antar Kannywood Yakubu Muhammed ya ce a shirye ya ke ya biya kudin karya yarjejeniya da masu shirya fim din mai taken: ‘‘fatal Arrogance’’, matukar su ka amince za su cire bangaren da ya fito a cikin fim din.

A wani zantawa da gidan rediyo BBC Yakubu Muhammed ya ce yayi matukar nadama da ya amince ya fito a cikin fim din.

Ya ce tuni ya sanar da mai shirya fim din cewa ya cire bangaren da ya fito a ciki, kuma a shirye yake ya biya kudin karya ka’idar yarjejeniyar kwantitagi.

.
Yakubu Muhammed ya kuma ce sam kokadan bai san cewa wasu daga cikin sashe na fim din zai kasance kamar yadda ya gani daga bisani ba.

YaKUBU Muhammed dai ya fito sau shida a cikin fim din wanda kuma aka harbeshi har ya mutu.

Fim din da aka fara fitar da tallansa ya bayyana yadda rikici ya kaure tsakanin mabiya shi’a da sojoji a garin Zari’a da ke jihar Kaduna.

A cewar Yakubu Muhammed, tun farko labarin fim din bai ga inda ya ke da alamar cin zarafin addini ba, sai dai daga bisani yaga sabbin abubuwa wadanda basa ciki tun da fari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!