Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Dan Hisba ya ki karbar rashawa

Published

on

Wani Jami’in hukumar Hisba mai suna Nuhu Muhammad Dala, ya ki amincewa da karbar cin hancin naira 100,000 daga hannun wani matashi mai sana’ar sayar kayan maye da nufin rufa masa asiri.

jami’in Hisban, wanda shi ne mataimakin kwamandan hukumar na karamar hukumar Dala, ya ki karbar cin hancin ne daga ‘yan uwan matashin wanda kwararre ne wajen sayar da kayan maye inda kuma ya kama shi da su dumu-dumu.

‘yan uwan matashin dai sun bukaci da a boye labarin kama kayan mayen ne inda suka bashi tsabar kudin, shi kuma da karbarsa sai ya sanar da hukumar.

A zantawar Freedom Radio da mataimakin kwamandan hukumar ta Hisba na jihar Kano mai kula da ayyuka na musamman Malam Shehu Tasi’u Ishaq, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin tare da cewa za’a hada mai laifin da kuma kudin da suka bayar a kuma gurfanar da su a kotu.

Malam Shehu Tasi’u Ishaq, ya kuma yaba wa jami’in nasu bisa namijin kokarin nasa na kin sakin kayan mayen.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!