Labarai
Ghana ta karbi ‘yan Najeriya da Amurka ta kora

Ghana ta tabbatar da isowar kashin farko na ‘yan Yammacin Afirka da aka kora daga Amurka a ƙarƙashin yarjejeniyar da ke tsakanin ƙasashen biyu.
Shugaba John Mahama, wanda ya tabbatar da hakan a lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a fadar gwamnatin ƙasar Jubilee House ranar Laraba, ya ce mutum 14 ne jirgin sama ya kai ƙasar a wani ɓangare na yarjejeniyar.
Yawancinsu ‘yan Nijeriya ne, yayin da ɗaya daga cikinsu ɗan ƙasar Gambiya ne.
You must be logged in to post a comment Login