Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

gobara ta kone ta kone shagunan sayar da abinci a kwalejin kimiyya da fasaha ta Kano

Published

on

Wata gobara da ta tashi a kwalejin kimiyya da fasaha ta jihar Kano ta kone shagunan sayar da abinci da sauran kayayyaki tare da haddasa asarar dukiya mai tarin yawa.

Shaidun gani da ido sun ce gobarar ta tashi ne a daren larabar da ta gabata bayan sallar Magriba a bangaren masu sayar da abinci na makarantar dake titin Yahya Gusau.

A cewar su, sun hango tashin hayaki ne kafin daga bisani wutar ta bazu zuwa sassan kantinan sayar da abincin da sauran kayan masarufin kwalejin.

wasu daga cikin masu gudanar da sana’ar sayar da abinci a makarantar wadanda gobarar ta lashe dukiyar su, sun bayyanawa Freedom Radio cewa gobarar ta yi musu kazamar barna ta dukiyoyi da runfunansu.

A nasa bangaren, Daraktan Makarantar Dakta Musa Gambo, ya ce ya zuwa yanzu, ba a gano musabbabin tashin wutar ba.

Daga bisani an samu nasararkashe  wutar da taimakon jami’an hukumar kashe gobara ta jihar Kano.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!