Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gobe Litinin za a yi jana’izar Mai Babban Ɗaki

Published

on

Fadar mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ta ce, za a yi jana’izar marigayiya Mai Babban Ɗaki a gobe Litinin 26 ga watan Afrilun da muke ciki.

Za a yi jana’izar da ƙarfe 11 na safe.

Wannan na cikin wata sanarwa da Madakin Kano Alhaji Yusuf Ibrahim Chigari ya fitar a ranar Lahadi.

Sanarwar ta ce, ana tsammanin isowar mamaciyar filin jirgin saman Malam Aminu Kano a yau Lahadi bayan sallar magariba.

Sanarwar ta kuma ce, za a kai mamaciyar hubbaren Gidan Sarkin Kano.

Muna addu’ar Allah ya gafarta mata, ya yi mata rahama tare da magabatan mu, da dukkan musulmai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!