Connect with us

Labarai

Goodluck Jonathan ya isa birnin Accra don halartar taro

Published

on

Tsohon Shugaban Ƙasar nan  Goodluck Jonathan, ya isa birnin Accra, na Ƙasar Ghana, domin halartar taron Dumokaradiyya na  Democracy Dialogue na 2025  da Gidauniyar sa ta shirya tare da haɗin gwiwar gwamnatin ƙasar.

Taron na bana, mai taken “Dalilan Da Ke Sa Dimokuraɗiyya ta mutu”, zai haɗa shugabanni da masana don tattauna ci gaba, ƙalubale, da makomar dimokuraɗiyya a Yammacin Afirka.

Jonathan ya ce yana fatan wannan tattaunawa za ta ƙarfafa dimokuraɗiyya a yankin tare da kawo zaman lafiya, tsaro da kyakkyawan shugabanci.

Taron ya zama muhimmin dandali a kowace shekara a Yammacin Afirka da yake  tattauna makomar dimokuraɗiyya, inda a baya ya kan jawo ’yan siyasa, ƙungiyoyi, da abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa.

A wannan karon ana sa ran waɗan da za su halarci taron za su tattauna muhimman batutuwa da suke damun yankin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!