Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Ƙetare

ECOWAS zata gudanar da taron gaggawa kan juyin mulki

Published

on

Shugabanin kungiyar kasashe mambobin kungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen yammacin Afrika ta ECOWAS ko kuma CEDEAO, za su gudanar da wani taron gaggawa a gobe Lahadi game da juyin mulkin da sojoji suka yi a Nijar.

Shugaban kasar nan,kuma sabon shugaban kungiyar Bola Ahmed Tinubu,shine zai jagoranci zaman wanda za a gudanar a babban birnin tarrayayyar Abuja.

Cikin wata sanarwa, Shugaba Tinubu ya yi Alla-wadai da juyin mulkin, inda kuma ya yi wa al’ummomin kasashen waje alkawarin cewa zai yi duk mai yiwuwa domin kare dimokuradiyya da kuma tabbatar da dorewar kyakkyawan shugabanci a yankin.

Shugaba Tinubu ya kuma yi fatan wannan taron na su zai samar da matsaya guda wadda za ta ba da damar mayar da Jamhuriyar Nijar kan turbar dimokuradiyya

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!