Connect with us

Labarai

Gwamna Abba Kabir ya buƙaci NBC ta fara tantance kafafen yaɗa labarai na Internet

Published

on

Gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bukaci hukumar da ke kula da kafafen yada labarai ta kasa NBC ta fara tantance kafafen yada labaran Internet.

Gwamnan ya yi wannan kira ne yayin da yake jawabi a taron da Hukumar NBC ta shirya a birnin Legas, wanda ya hada masana, masu ruwa da tsaki da kuma shugabannin kafafen yada labarai, inda ya ce ya kamata NBC ta fara tantance kafafen rediyo da talabijin na intanet don dakile yada labaran karya da kalaman batanci a kafafen sadarwa.

Gwamnan wanda Daraktan yada labaransa, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya wakilta, ya nuna damuwa kan yadda wasu kafafen intanet ke yada labarai marasa tushe musamman wadanda ke da nasaba da addini ko siyasa.

To sai dai tun a baya NBC ta sha bayyana cewa dokarta ba ta bata wannan damar ta tantance kafafen rediyo da talabijin na intanet ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!