Connect with us

Labarai

Gwamna Abba Kabir ya tafi Saudiyya don halartar jana’izar Aminu Dantata

Published

on

Gwamnan jihar Kano  Abba Kabir Yusuf ya tashi daga filin jirgin sama na Malam Aminu Kano tare da manyan jami’an gwamnati domin halartar jana’izar marigayi Alhaji Aminu Alhassan Dantata. 

 

Mai magana da yawun gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ne ya tabbatar da hakan biyo bayan wallafa labarin a shafinsa na Facebook.

 

Tawagar da ta tafi zuwa jana’izar ta haɗa data  Gwamnan jihar Jigawa  Umar Namadi da Khalifa Muhammadu Sanusi II. 

 

Haka zalika akwai tsohon gwamnan Jigawa, Ali Sa’ad Birnin Kudu, da wasu manyan sarakuna da jami’an gwamnati daga Kano da Jigawa. 

 

Daga cikin wadanda suka shiga tawagar har da Galadiman Kano,sai Matawallen Kano, da Sarkin Yakin Kano, sai  Injiniya Sagir Koki, Nastura Ashir Sharif, Alhaji Sabiu Bako. 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!