Connect with us

Labarai

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya saki fursunoni mata 8

Published

on

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya saki mata fursunoni takwas daga gidan gyaran hali na Goron-Dutse, inda ya biya musu tara da kuma basussukan da ake binsu.

Daga cikin matan da aka sako, hadda mata masu juna biyu da kuma wasu biyu da ke shayar da jarirai.

Gwamnan ya ɗauki wannan mataki ne yayin wata ziyarar bazata da ya kai gidan gyaran halin tare da wasu manyan jami’an gwamnatinsa.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ya bayyana manufar ziyarar da duba yanayin da fursunonin ke ciki da kuma gano hanyoyin da gwamnati za ta tallafa musu bayan sun fita daga gidan..

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!