Connect with us

Labaran Kano

Gwamna Abba zai koma APC a gobe Litinin

Published

on

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf zai koma jam’iyyar APC, mai mulkin kasa a gobe Litinin 26 ga watan Janairun 2026.

A ranar Juma’a ne gwamnan ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyarsa ta NNPP, saboda abin da ya bayyana da rikicin cikin gida da ke addabar jam’iyyar, 

Cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a jiya Lahadi, ya ce gwamna ya yanke shawarar komawa tsohuwar jam’iyyarsa ta APC bayan tuntuɓar abokan shawararsa na siyasa da sauran masu ruwa da tsaki.

Abba Kabir Yusuf ya taɓa shiga APC a 2014, in da ya ce sake komawa APC zai ƙara ƙarfafa alaƙa mai ƙarfi tsakanin gamnatin jihar da ta tarayya, wani abu da sanarwar ta ce zai samar wa jihar ci gaba da ƙarfafa tsaro da inganta ci gaban jihar.

Sanarwar ta ƙara da cewa a ranar Litinin ɗin gwamnan zai karɓi katin jam’iyyar APC tare da wasu ƴan majalisar dokokin jihar 22 ciki har da kakakin majalisar, da ƴanmajalisar tarayya takwas da shugabannin ƙananan hukumomi 44.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!