Connect with us

ilimi

Gwamna Namadi ya bude Makaranta ta musamman a Garki

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce, ta kashe sama da Naira miliyan dubu biyar wajen ginawa tare da sanya kayan aiki a Sabuwar makarantar Sakandire ta musamman da ke garin Garki domin koyar da ilimi da kuma Sana’oin dogaro da kai ga dalibai.

Da ya ke gabatar da jawabi a wurin taron bude makarantar, gwamnan jihar Malam Umar Namadi, ya ce, makarantar ta na daga cikin makarantun Sakandire na musamman guda takwas da gwamnatinsa za ta samar a sassan jihar.

A nasa jawabin, kwamishinan ilimi mai zurfi na Jigawa Farfesa Isah Yusuf chamo ya ce, an zabo daliban makarantar ne bisa cancanta bayan sun samu nasara a jarawar da aka shirya musu har sau uku.

Kwamishinan, ya kara da cewa, bude makarantar wani bangare ne daga cikin shirin gwamnati da jama’a karo na takwas a karamar hukumar ta Garki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!