Connect with us

Labarai

Gwamna Radda ya jagoranci takwarorinsa wajen ganawa da babban hafsan soji

Published

on

Gwamnan jihar Katsina kuma shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa maso Yamma, Malam Dikko Umaru Radda, ya jagoranci wasu gwamnonin yankin wajen ganawa da babban hafsan sojin Najeriya Janar Christopher Musa, a shalkwatar tsaro ta ƙasa da ke Abuja.

 

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan Katsina, Ibrahim Kaulaha Muhammad, ya fitar.

 

Sanarwar ta bayyana cewa taron na sirri ya mayar da hankali ne kan tsare-tsare da ƙarfafa ayyukan tsaro a Arewa maso Yamma, musamman ganin nasarorin baya-bayan nan da dakarun soji suka samu kan ‘yan bindiga a yankin.

 

Cikin tawagar da Dikko Radda ya jagoranta har da Gwamnan Zamfara Dauda Lawal da mataimakin gwamnan Sokoto Alhaji Idris Mohammed Gobir da sakataren gwamnatin jihar Kebbi Alhaji Yakubu Bala.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!