Connect with us

Addini

Gwamna Radda ya kaddamar da taron addu’o’i kan matsalolin tsaro

Published

on

Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya kaddamar da shirin addu’o’i na musamman tare da malamai da shugabannin addini da masu rike da sarautun gargajiya domin neman taimakon Allah kan matsalolin tsaro da jihar ke fuskanta.

 

Wata sanarwra da mai magana da yawun gwamnan, Ibrahim Kaula Mohammed, ya fitar ce ta bayyana hakan.

 

Sanarwar ta ce, taron ya haɗa malamai da shugabannin al’umma da jami’an gwamnati daga sassa daban-daban na jihar, inda aka gudanar da addu’o’i ga waɗanda suka rasa rayukansu sakamakon matsalar tsaro tare da roƙon Allah ya ci gaba da bai wa jihar kariya daga matsalolin tsaro.

 

Gwamna Radda ya ce, matsalar tsaro ba ta da alaƙa da addini ko siyasa, inda ya jaddada cewa haɗin kai da hakuri su ne ginshiƙai wajen magance ta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!