Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamna Yari na yaki da batun karin mafi karancin albashi domin kare kuskuren sa

Published

on

Kungiyar ma’aikatan kananan hukumomi ta kasa NULGE ta ce gwamnan jihar Zamfara Abdulazeez Yari na yaki da batun karin mafi karancin albashi ne domin kare kuskuren da ya tafka na kin biyan ma’aikatansa mafi karancin albashi na naira dubu 18 da ya yi.

Shugaban kungiyar ta kasa Kwamared Ibrahim Khalil ne ya bayyana hakan ga manema labarai, inda ya ce ma’aikata a jihar Zamfara na daukar naira dubu shida ne kawai a matsayin mafi karancin albashi.

Ya kuma ce mafiya yawan tashin hankulan da ke faruwa a jihar Zamfara na da nasaba da karancin kudaden da ma’aikatan ke dauka a matsayin albashi.

Kwamared Ibrahim Khalil ya ce matukar ma’aikata basu samu kudaden da ya da ce da za su iya kula da kan su ba, shakka babu, ba tayyada za a samu zaman lafiya a jihar.

Ya kuma koka kan yadda ma’aikatan jihar Zamfara suka zama koma baya a kasar nan ta fuskar kula da walwalar su, inda ya ce a jihar filato baya ga naira dubu 18 da ta ke biya a matsayin mafi karancin albashi, su kan su kananan hukumomin na karawa ma’aikatan su dan wani abu.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!