Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ganduje: Babu tabbacin ko za mu iya biyan dubu 30,600 ga ma’aikata a watan Afrilu

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce babu tabbacin ko za ta biya mafi karancin albashi na naira dubu talatin da dari shida ga ma’aikatan jihar a wannan wata na Afirilu.

Gwamnan Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje wanda kwamishinan yada labarai na jihar Kano kwamared Muhammed Garba ya wakilta, shine ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai, bayan kammala taron da kungiyar kwadago ta kasa (NLC) ta shirya a ranar juma’a a Kano.

Sai dai ya ce har yanzu gwamnatin Kano ba ta sauya matsaya ba kan biyan naira dubu talatin da dari shida ga ma’aikata a matsayin mafi karancin albashi, amma hakan ya danganta ne kawai ga yadda ta samu kasonta na rabon arzikin kasa daga asusun tarayya.

A nasa bangaren shugaban kungiyar kwadago ta kasa (NLC) reshen jihar Kano kwamared Kabiru Ado Munjibir, ya ce, gwamnati ta yi musu alkawarin biyan dubu talatin da dari shida idan aka samu isassun kudade daga asusun tarayya.

Ya kuma ce kungiyar za ta ci gaba da gwagwarmaya don kare muradun ma’aikatan jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!