Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami’anta 23 a harin Metele

Published

on

Rundunar sojin kasar nan ta tabbatar da mutuwar sojojin ta 23 inda kuma wasu 31 suka samu raunuka bayan da mayakan Boko Haram suka kai hari a sansanin su da ke Metele a ranar 18 ga watan Nuwambar nan da muke ciki.

Sai dai wannan adadi ya saba da adadin da rahotannin suka bayyana a baya cewa ana zargin mayakan sun kashe sojin daga 44 zuwa dari ne.

Cikin wata sanarwa da Birgediya Janar Sani Usman ya fitar a madadin babban hafsan sojin kasar nan Laftanal Janar Tukur Buratai ta ce a tsakanin 2 ga watan Nuwamba zuwa 17 ga watan, yan Boko Haram sun kai hari kan sojin kasar nan a kauyukan Kukawa da Ngoshe da Kareto da kuma Gajiram.

Ya kuma ce dukkanin hare-haren, rundunar sojin ta kawar da su, sai dai an kashe sojoji goma sha shida inda kuma 12 suka samu raunuka, yayin dauki ba dadin.

Ta cikin sanarwar Sani Usman ya ce al’amarin da ya faru a ranar 18 ga watan, ya faru ne a dai-dai lokacin da rundunar sojin kasar nan ke tsaka da shirye-shiryen babban taron hafsan sojojin kasar nan da aka tsara gudanarwa a garin Benin na jihar Edo.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!