Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kano:Majalisar dokokin jihar ba ta da ikon bincikar Gwamna Abdullahi Ganduje

Published

on

A yau Alhamis ne babbar kotun jihar Kano ta yanke hukuncin cewa majalisar dokokin jihar Kano ba ta da iko, ko hurumin gayyata ko kuma bincikar gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje kan zargin karbar na goro a hannun ya kwangila.

 

Kotun karkashin jagoranci mai shari’a Ahmad Tijjani Badamasa ta yanke hukuncin cewa ikon bincikar manayan laifuka na wuyan hukumar Yan Sanda ne ko kuma hukumar EFCC ko ICPC.

 

Mai shari’a A T Badamasi ya ce ikon da tsarin mulkin kasa ya bawa majalisar dokokin jiha, shi ne kawai su samar da doka su kuma tabbatar da doka na aiki, amma basu da ikon bincikar manyan laifuka.

 

Jim kadan bayan yanke hukuncin ne lauyan wadanda suka shigar da kara Barrister Nuraini Jimoh ya yaba da kokarin kotun na yanke hukuncin, inda kuma lauyan wadanda ake kara Barrister Muhammad Waziri ya ce zai tattauna da wadanda ya ke karewa domin daukar mataki na gaba.

 

Wakilin mu Muhammad Bashir Inuwa ya ruwaito wadanda ake karar sun hadar da majalisar dokokin jihar Kano da kuma shugaban kwamitin binciken na majalisar Baffa Babba Danagundi ta kuma attorney janar na jihar Kano.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!