Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano zata kashe fiye da Biliyan 11 wajen magance zaizayar kasa

Published

on

Gwamnati jihar Kano zata kashe fiye da biliyan Goma sha daya wajen magance zaizayar kasa da samar da titi a yankin Gayawa, Bulbula da wasu gurare cikin karamar hukumar Ungoggo.

Gwamna Injiniya Abba Kabir Yusif, ne ya bayyana hakan  lokacin da yake mika diyar kudi ga mutanen da aikin ya shafi gidajensu.

Gwamnan ya kara da cewa Gwamnati zata tabbatar da biyan duk Wanda aikin ya shafa diyya kafin  farawa  inda za a fara da raba miliyan dari shida ga wasu cikin mutane da aikin zai shafa dan samun sabon matsuguni.

Ya kuma kara da cewar Gwamnatin sa zata ci gaba da bibiyar duk inda zaizayar kasa take a fadin jihar Kano dan daukar matakin da ya kamata.

Kwamishinan Muhalli na jihar Kano Dakta Dahiru Muhammad Hashim, ya ce aikin zai shafi gidaje fiye da dari biyu kuma Gwamnati tayi kyakkyawan tsari wajen biyansu diyya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!