Jigawa
Gwamnatin jigawa na yi wa ma’aikata rijista a shirin asusun kiwon lafiya
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2020/05/Gov-Badaru-Jigawa.jpg)
Gwamnatin jihar Jigawa, ta fara yi wa ma’aikatan jihar rijistar shirin Asusun kiwon Lafiya bayan sanya hannu kan dokar shirin da gwamnan jihar Alhaji Muhd Badaru Abubakar ya yi, tun a bara.
Babban Sakataran zartarwar hukumar asusun kiwon Lafiya ta jihar Jigawa Dr. Nura Ibrahim Salisu ne ya bayyana haka ga manema labarai, jim kadan bayan fara yin aikin rijistar a gidan Gwamnatin jihar Jigawa.
Ku saurari wakilinmu daga Dutsen Jihar Jigawa Muhd Aminu Umar Shuwajo a cikin jerin labaru na nan gaba.
You must be logged in to post a comment Login