Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamnatin Jigawa ta rage wa ma’aikata lokacin aiki

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa ta rage wa ma’aikatan jihar lokacin aiki na awanni 2 a yayin watan azumin Ramadana mai girma na wannan shekara ta 2019.

Mai Magana da yawun ofishin shugaban ma’aikata na  jihar ta Jigawa Alhaji Isma’il Ibrahim  ya bayyana hakan a birnin Dutse a jiya Talata 7 ga watan Mayu ta cikin wata sanarwa da ya fitar aka rabawa manema labarai.

A cewar Alhaji Isma’ila Ibrahim a halin yanzu ma’aikatan jihar za su je wuraren aiki ne da misalin karfe 9 na safiya su kuma tashi da misalin karfe 3 na yamma a tsakanin ranakun Litinin zuwa Alhamis maimakon su je wuraren ayyukan su da misalign karfe 8 su kuma tashi karfe 5 na yamma.

Mai Magana da yawun ofishin shugaban ma’aikatan ya kuma yi bayanin cewar, makasudun daukar wannan mataki shi ne, domin baiwa ma’aikatan jihar damar bautawa Allah a yayin azumi da kuma yin bude baki akan lokaci.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!