Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kaduna ta gargadi makarantu masu zaman kansu su guji karin kudin makaranta

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta gargadi makarantu masu zaman kansu a jihar da su guji yin karin kudin makaranta ba tare da sahalewar gwamnati ba.

 

Cikin wata sanarwa da babbar darakta mai kula da makarantu masu zaman kansu a ma’aikatar ilimin jihar, Mercy Bainta Kude ta fitar, ta ce gwamnati ba ta amince da yin karin kudin makaranta ba tare da saninta ba.

 

Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da aka koma zangon farko na sabuwar shekarar karatu ta 2025 zuwa 2026.

 

A cewar sanarwar bai kamata makarantun su kara kudin ba, a daidai lokacin da gwamnatin jihar ke shirin rage kudin makaranta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!