Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin jihar Kano zata inganta gidan zoo – Ranar yawon buɗe ido ta duniya

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce za ta inganta gidan adana namun daji na jihar domin ƙara samun baƙi masu shigowa daga sassa daban-daban.

Kwamishinan ma’aikatar al’adu da yawon buɗe ido na jihar Alhaji Ibrahim Ahmad ƙaraye ne ya bayyana hakan, a wani ɓangare na bikin ranar yawon buɗe ido da ake gudanarwar kowacce shekara.

Ahmad ƙaraye ya ƙara da cewa tuni dokoki suka yi nisa wajan tabbatar da da gyara harkokin yawon buɗe ido da kuma al’adu.

“Zamu tabbatar da dokar hana shan shisha a wuraren shaƙatawa da kuma ƙananan yaran da suke zuwa hotel, sai kuma masu zuwa gidan biki da baƙin gilashin mota, tare da kaiwa dare a wajan bikin” in ji Kwamishinan.

Majalisar ɗinkin duniya ce ta ware ranar 27 ga watan satumbar kowacce shekara domin tunawa da irin muhimmancin da yawon buɗe ido ke dashi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!