Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Gwamnatin Katsina ta sanar da ranar komawar ɗalibai makaranta

Published

on

Gwamnatin jihar Katsina ta sanar da ranar uku ga watan Oktoba a matsayin ranar da makarantun gwamnati da masu zaman kan su za su koma karatu a fadin jihar.

Wannan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ma’aikatar ilimi ta jihar Malam Sani Danjuma ya fitar.

A cewarsa, komawa makarantar zai bada dama wajen cike gurbin zangon karatu na uku na shekarar 2020 da 2021 musamman a yankunan da suke fuskantar matsalar tsaro a jihar.

Sanarwar ta ce, kwamishinan ilimin jihar Dakta Badamasi Lawal ya tabbatar da cewa dukannin daliban makarantun kwana da jeka-ka-dawo za su ci gaba da karatu a ranar 4 ga watan Oktoba.

Tun da fari dai an tsara komawar dalibai makaranta a jihar a ranar 13 ga watan Satumbar da muke ciki, sai dai an ɗage shi ne don daidaita jadawalin karatu

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!