Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jihar Kano ta jaddada kudirinta na magance matsalar karancin gidaje

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta sake jaddada kudirinta na magance matsalar karancin gidaje da ke addabar al’ummar jihar.

Kwamishinan gidaje da ci gaban birane na jihar Kano, Arc. Ibrahim Yakubu Adamu, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manyan jami’an ma’aikatar. 

Arc Adamu ya bayyana cewa tun bayan samar da ma’aikatar, ta gano wuraren da za a aiwatar da aikin samar da gidaje karkashin jagorancin Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf, da suka hadar da garin Lambu cikin karamar hukumar Tofa, da Yargaya a karamar hukumar Dawakin Kudu, 

Da kuma kammala ayyukan gidajen Kwankwasiyya da Amana da kuma Bandirawo.

Hakan yasa, kwamishinan ya shawarci manyan ma’aikatan ma’aikatar da su kasance masu tunani na aiki tare domin cimma muradun gwamnati na ci gaban jihar Kano.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!