Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Kano zata sauya  fasalin samar da gidaje

Published

on

Gwamnatin Kano ta ce zata maida hankali wajen samar da gidaje a jihar nan.

Sabon kwamishinan gidaje da sufuri na jihar Kano Barrister Musa Abdullahi Lawan ya bayyana hakan ga manema labarai jim kadan bayan kama aiki.

Barrister Musa Abdullahi Lawan ya ce zai yi aiki da kudororin gwamnatin Ganduje wanda zai inganta rayuwar ‘yan jihar Kano.

“Zamu yi duk mai yuwa wajen inganta samar da karancin gidaje da kuma gina rukunin gidajen a nan Kano don wadata ‘yan asalin jihar nan da gidaje a cewar sa”

Muna rokon gwamna Ganduje ya sulhunta Muntari da Sha’aban –Habib Sadam

Ganduje da Sarkin Kano sun gana da masu zuba jari daga kasar China

Ganduje ya hana iyayen yara Magana da yan jarida
Ka zalika sabon kwamishinan ya ce Allah ya wadata jihar nan da filaye kasancewar hakan ya sanya masu zuba jari ke tururuwa don zuba jari a nan Kano.

Ya kuma yi alkawarin sake nazari kan harkokin sufuri a jihar nan wanda zai yi dai-dai da na zamani

Har ila yau, Barrister Musa Abdullahi ya ce za’a samar da kayan sawa na bai daya ga masu harkokin sufuri da kuma fantin mota ta yadda jihar Kano zata yi gugayya da sauran kasashen waje ta fuskar sufuri.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!