Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Gwamnatin jihar Legas ta dakatar da bikin ranar yancin kai

Published

on

Gwamnatin jihar Lagos ta soke bikin ranar yancin kan Najeriya, sakamakon annobar Covid-19.

Gwamnan jihar Babajide Sanwo-Olu wanda ya bayar da umarnin a wata sanarwa da ya fitar ya ce an soke bukukuwan da ake yi a irin wannan ranar ne da suka hadar da fareti domin kaucewa taruwar jama’a sama da hamsin.

Ya ce jihar ta zabi soke yi bikin murnar zagayowar ranar yancin kan ne saboda kaucewa yaduwar cutar COVID-19.

Gwamnan ya taya mazauna jihar murnar wannan rana inda ya shawarce su da su yi bikin cikin nutsuwa a gida tare da yi wa kasa addu’a.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!