Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za’a bude makarantu a jihar Katsina

Published

on

Gwamnatin jihar Katsina ta ayyana ranar 5 ga watan Oktoba a matsayin ranar da za’a bude makarantun sakandire da na firimare masu zaman kansu da na gwamnati a fadin jihar.

Kwamishinan ilimi na jihar Badamasi Lawal ne ya bayyana haka, a wata hira da manema labarai, inda ya ce za a fara bitar darussan zango na biyu da zarar an makarantun.

Ya kuma ce, bayan an kammala bitar karatun sai kuma a fara gudanar da jarabawar karshen zangon na biya a ranar 19 zuwa 23 na watan na Oktoba.

“Daliban za su dawo makaranta don ci gaba da zango na uku wanda za a fara a ranar 26 ga watan Oktoba zuwa ranar 24 ga watan Janairun shekarar 2021, sai a gudanar da jarabawa daga ranar 25 ga watan Janairun a kuma kammala ranar 5 ga watan Faburairu.” In ji shi.

Ya ce ya zama wajibi dalibai da kuma malamai su yi amfani da takunkumin rufe fuska tare da kiyaye ka’idojin bada tazara domin kariya daga cutar Corona.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!