Connect with us

Labaran Kano

Gwamnatin Kano ta bayyana gamsuwar ta da zabukan cike gurbi da aka yi

Published

on

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yaba da yadda aka  gudanar da zaben cike gurbi a jihar ba tare da tashin hankali ko magudi ba.

Gwamnan Ya bayyana hakan ne bayan kammala zaben cike gurbi da hukumar zabe mai zaman kan ta ta kasa INEC ta shirya a mazabun Kano Municipal da Ungogo na majalisar dokokin jihar.

Inda  ya bayyana cewa yanzu zamanin  tayar da hankali yayin kada kuri’a ya wuce, yana mai jaddada cewa zaben na wannan karon ya gudana ba tare da rikici ko amfani da makamai ba, haka kuma ba a samu wata alamar magudi a zaben  ba.

Sannan ya yabawa jami’an tsaro da ma’aikatan INEC kan yadda suka gudanar da aikinsu, yana mai cewa hakan ya taimaka wajen tabbatar da sahihin zabe.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!