Labarai
Gwamnatin kano ta ce za ta magance matsalar zaizaiyar kasa a faɗin jihar

Gwamnatin kano ta ce za ta tabbatar da magance duk wata matsalar Zaizayar ƙasa a dukkannin yankunan dake fama da matsalar a faɗin jihar, musamman a wannan lokacin na ƙaratowar damuna domin kare al’umma daga barazanar ambaliya.
Babban Sakataren a hukumar kula da sauyin yanayi da Zaizayar ƙasa na jihar kano Dakta Muhammad S Khalil ne ya bayyana hakan, ya ce gwamnati za ta kawo karshen matsalar a wasu yankunan na jihar kano.
Ya kuma ce nan bada jimawa bane gwamnatin za tayi duk mai mai yuwuwa domin ganin ta shawo kan matsalar a cikin birni da kewaye musamman inda matsalar tafi kamari.
You must be logged in to post a comment Login